Isa ga babban shafi
Nigeria

Biafra: Yadda al'amura suka kasance a kudancin Najeriya

Kasuwanni da makarantu sun kasance a rufe a yankin kabilar igbo, da ke kudu maso gabashin Najeriya bayan kungiyoyin da ke fafutukar kafa kasar Biafra suka yi kira ga jama’ar yankin da su kasance a gida, yayinda ake cika shekaru 50 da Chukwuemeka Ojukwu ya kaddamar da yakin neman tabbatar da kasar Biafra.

Nnamdi Kanu, shugaban gwagwarmayar neman kafa Biafra.
Nnamdi Kanu, shugaban gwagwarmayar neman kafa Biafra. STRINGER / AFP
Talla

Kasuwanni dai sun kasance a rufe a biranen Enugu da Owerri da kuma Aba, yayinda kuma bankuna suka kasance a rufe, illa wasu ma’aikatan da ke gudanar da ayyukansu a cikin ofisoshi.

Muhammad Lawal dan Tibi mazauni a garin Enugu, kuma mai magana da yawun ‘yan arewa mazauna yankin na kudu maso gabashin Najeirya, yayinda zantawarsa da RFI Hausa, ya ce ba’a samu tashin hankali a garin ba.

Sai ma wasu daga cikin shugabannin Coci da suka yi wa shugaban Najeriya addu’ar samun lafiya, da kuma bayyana cigaba da neman kafa kasar Biafra a matsayin koma baya ga yankin.

00:52

Biafra: Yadda al'amura suka kasance a kudancin Najeriya

Nura Ado Suleiman

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.