Najeriya
INEC ta yi watsi da bukatar dage zaben jihar Ondo
Hukumar Zabe a Najeriya taki amincewa da bukatar Jam’iyyar PDP na dage zaben Gwamnan Jihar Ondo da ake shirin yi a karshen wannan mako.
Wallafawa ranar:
Talla
Jam’iyar PDP ta bukaci dage zaben ne dan bai wa kotun koli damar yanke hukunci kan takaddamar tsayar da dan takara.
Hukumar zaben tace Jam’iyyu 28 suka tsayar da ‘Yan takara a zaben, saboda haka ba za ta dage zaben ba saboda bukatar Jam’iyyar PDP.
A ranar 26 ga wannan watan na Nuwamba za a gudanar da zaben.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu