PDP ta bukaci a dage zaben gwamnan Jihar Ondo
Jam’iyyar PDP da ke adawa a Najeriya ta bukci hukumar Zabe ta dage zaben gwamnan Jihar Ondo da za a gudanar a ranar 26 ga wannan watan nan Nuwamba har sai kotu ta tabbatar da dan takarar jam’iyyar tsakanin Eyitayo Jegede da Jimoh Ibrahim.
Wallafawa ranar:
PDP ta nemi dage zaben ne saboda rikicin Jam’iyyar inda mutane biyu ke ikirarin zama ‘Yan takara gwamnan Jihar ta Ondo.
Wannan kuma na zuwa ne bayan kotun daukaka kara a Abuja ta dage zartar da hukunci akan koken da Eyitayo Jegede ya shigar na tabbatar da shi a matsayin dan takarar gwamna sabaniin Jimoh Ibrahim da kotun Tarayya ta tabbatar a matsayin dan takarar gwammnan na PDP.
Jimoh Ibrahim dai na bangaren shugabancin Senata Ali Modu sheriff, yayin da Jegede ke bangaren Senata Ahmed Makarfi da ke hamayya da Sherif a shugabancin Jam’iyyar na kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu