Za a gurfanar da masu almubazzaranci a NNPC-Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buahari ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba, za a gurfanar da wadanda suka yi almubazzaranci da biliyoyin kuadade mallakan Kamfanin mai na Kasar, NNPC.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Buhari ya fadi haka ne a ganawar da ya yi da shugaabn Kasar China Xi Jinping a jiya lahadi a birnin New York na kasar Amurka.
Buhari ya kara da cewa gwamantinsa a shirye take domin tabbatar da tsafta a Kamfanin NNPC ta yadda zai kubuta daga matsalar cin hanci da rashawa.
To sai dai shugaban na Najeriya bai sanar da lokacin da za a gurfanar da wadanda ake zarigi da almubazzaranci da kudaden ba.
,
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu