Najeriya
‘Yan bindiga sun kai hari a Argungu na Najeriya
Rahotannin da ke fitowa daga Argungu a jahar kebbin Najeriya na cewa, a cikin daren jiya Alhamis wasu mahara sun kai farmaki a garin inda suka kashe mutane biyu tare da wawushe kudaden da ba'a kai ga gano adadin yawansu ba.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani mazaunin garin ya shaidawa wakilin RFI Hausa Hassan Sanyinnawal cewa, maharan wadanda yawansu ya kai takwas sun zo ne akan babura kuma an yi nasarar kama mutun daya a cikinsu sakamakon take shi da mota da wani ya yi.
Kakakin ‘Yan Sandan Jahar kebbi Bala Sule ya tabbatar da kai harin tare da cewa an kashe Dan sanda guda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu