Isra'ila ta yi luguden wuta a kan wani asibitin kudancin Gaza
Kungiyar agaji ta Red Crescent ta zargi Isra’ila da kai hari da jirgi mara matuki a kan wani asibiti a birnin Khan Younis, a Juma’a, a daidai lokacin da hare-haren da ta ke ci gaba da kai wa kudancin Zirin Gaza ke barazana ga cibiyoyin lafiyar da ke aiki har yanzu a yankin da rikicin ya daidaita.
Wallafawa ranar:
Mutane da dama ne suka ji rauni sakamakon luguden wutar da jirage mara matuki na Israila suka kai asibitin Al-Amal da ma shelkwatar kungiyar agajin.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana nazari a kan wannan rahoto.
A kusa da wurin da aka kai harin jirgi mara matuki, rahotanni sun ce an hango tankuna yakin Isra’ila suna wucewa ta kusa da asibiti mafi girma da ya rage a yankin, wato Nasser, inda aka yi ta jink kararrakin harbe harbe da fashe-fashe, kana ganau suka ce an yi bata -kashi.
Isra’ila takadamar da wani gagarumin hari a kan Khan Younis a wannan makon da zummar kame birnin, wanda ta ce yanzu ya zama sheljwatar mayakan Hamas, wadanda suka kai mata hari a ranar 7 ga watan Oktoba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu