Isa ga babban shafi

Yakin Gaza: Amurka ta ce za ta ci gaba da taimaka wa Isra'ila da makamai

Amurka ta sha alwashin ci gaba da taimaka wa Isra’ila a yakin da taake  da Hamas, a yayin da kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta dage kuri’ar da ta kudiri aniyar kadawa a game da rikicin Gaza.

Sakaataaren tsaon Amurka Lloyd Austinda ministaan tsaron Isra'ila  ministre israélien  Yoav Gallant.
Sakaataaren tsaon Amurka Lloyd Austinda ministaan tsaron Isra'ila ministre israélien Yoav Gallant. © Violeta Santos Moura / Reuters
Talla

A yayin ziyarar da ya kai Isra’ila a Litinin din nan, sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin da ministan tsaron Isra’ila sun gudanar da wani taron manema labarai na hadin gwiwa, inda a nan ne ya yi kira ga karin agaji ga wadanda rikicin Gaza ya daidaita.

Sai dai Lloyd ya ce Amurka za ta ci gaba  da samar wa Isra’ila taimakon kayan yaki don ci gaba da kokarin kakkabe  mayakan Hamas, wanda suka ja daga tun bayaan harin 7 ga watan Octoba.

A waje daya kuma, majiyoyin diflomasiyya sun bayyana cewa an dage  kuri’ar da aka tsara kadawa a game da rikicin Gaza  a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zuwa wannan Talata, a yayin da ake ci gaba da tattauna  abubuwan da daftarin da za a yi aiki da shi a yayin kuri’ar zai kunsa.

Ya zuwa yanzu, akalla mutane dubu 19 da dari 4 da 53 ne suka mutu  tun da Isra’ila ta fara kai hare-hare zirin Gaza, kana, wadanda suka ji rauni sun kai dubu 52 da dari 2 da 86, a cewar mahukuntan Hamas.  

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.