Isa ga babban shafi

An yi mummunan artabu tsakanin mayakan Hamas da sojojin Isra'ila a Gaza

Kungiyar Hamas ta ce an yi mummunan artabu tsakanin mayakanta da sojojin Isra'ila jiya Lahadi a cikin arewacin Zirin Gaza.

Tankokin yakin Isra'ila a kan iyakar Zirin Gaza.
Tankokin yakin Isra'ila a kan iyakar Zirin Gaza. © Ohad Zwigenberg / AP
Talla

Wannan na zuwa ne a yayin da adadin Falasdinawan da suka rasa rayukansu a Gaza ya haura mutane dubu takwas, sakamakon hare-haren da Isra’ilar ke ci gaba da kaiwa.

Bayan shafe makwanni jiragen yakinta na ruwan bama-bamai ta sama, Isra'ila ta sanar da shiga sabon mataki a yakin da Firaminista Benjamin Netanyahu ya yi gargadin cewa zai kasance mai tsawo cike kuma da kalubale.

Da yammacin jiya Lahadi rundunar sojin Isra'ila ta fitar da wani faifan bidiyo da ke nuna yadda dakarunta na kasa hade da tankokin yakinsu ke kai samame a sassan arewacin Gaza.

Zirin Gaza
Zirin Gaza © Jack Guez / AFP

Sojojin dai sun yi ikirarin kai hare-hare sama da 450 kan cibiyoyin kungiyar Hamas na bayar da umarni, da na leken asiri, da kuma wuraren da take amfani da su wajen harba makamai masu linzami kan Isra’ila.

Kwanaki 23 da suka gabata ne dai a ranar 7 ga watan Oktoba, mayakan Hamas suka kaddamar da farmaki a cikin Isra'ila, lamarin da yayi sanadin mutuwar mutane fiye da dubu 1,400, yayin da suka yi garkuwa da wasu 239.

A sabbin alkaluman da ta fitar a baya bayan nan, ma’aikatar lafiyar Gaza ta ce ya zuwa yanzu yawan Falasdinawa da suka mutu a hare-haren Isra’ila ya zarce mutane dubu 8, rabinsu kuma yara ne kanana.

Motocin dakon kayan agaji na Masar yayin kokarin shigar da tallafi ga Falasdinawa a Zirin Gaza ta kan iyakar Rafah.
Motocin dakon kayan agaji na Masar yayin kokarin shigar da tallafi ga Falasdinawa a Zirin Gaza ta kan iyakar Rafah. AP - Mohammed Asad

Rayuwa a cikin Zirin Gaza dai na ci gaba da yi wa fararen hula kunci, lamarin da ya sa a karshen makon da ya gabata, dubban Falasdinawa suka afka wa rumbunan ajiyar Majalisar Dinkin Duniya a kokarinsu na samun abinci, da magunguna da sauran kayayyakin bukata.

Ana ci gaba da fuskantar karancin kayayyakin agaji a Gaza saboda takaita adadin motocin jin kan da ke shiga yankin daga iyakar Masar.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce a ranar Lahadin da ta  gabata, motoci 33 dauke da kayan agaji na ruwa da abinci da magunguna suka shiga yankin na Falasdinawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.