Isa ga babban shafi
Yemen

Saudiya ta sanar da kashe karin ‘yan tawayen Houthi 92 a Yemen

Dakarun kawancen da Saudi Arabia ke jagoranta sun sanar da kashe karin ‘yan tawayen Houthi 92 a wani sabon harin ta sama da suka kaddamar kan yankuna biyu dake birnin Marib a kasar Yemen.

Mayakan sa kai masu biyayya ga Saudiya a Yemen yayin fafatawa da 'yan tawayen Houthi a birnin Marib. 17 ga Oktoba, 2021.
Mayakan sa kai masu biyayya ga Saudiya a Yemen yayin fafatawa da 'yan tawayen Houthi a birnin Marib. 17 ga Oktoba, 2021. - AFP
Talla

‘Yan tawayen Houthin na baya bayan nan da suka halaka a baya bayan nan, na daga cikin cikin daruruwan da dakarun kawancen n a Saudiya suka sanar da kashewa a hare haren da suka kaddamar ta sama a birnin na Marib da kewaye.

Kamfanin dillancin labaran Saudiya ya ce bayan mutane 92 da aka kashe, dakarun sun kuma lalata motocin soji 16 a Yankin Al Jawba da Al Kassara.

A ranar Litinin 18 ga watan Oktoban da muke, kawancen sojojin da Saudiya ke jagoranci wajen yaki da ‘yan tawayen Houthi ya sanar da kashe mayakan Houthin 160 a hare haren sama da ya kai kan birnin Marib dake kudancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.