Isa ga babban shafi
RIKICIN GAZA

Shugaban Amurka Joe Biden, ya bayyana aniyar hana yahudawan dake cin zarafin Falastinawa Visa

Daukar matakin dai na Amurka  na zama irinsa na  farko da Amurka ta gabatar da barazanr amfani da  matakan ladaftar kan yahudawan yan kakagidan. Kamar yadda shugaban na Amuruka Joe Biden ya sanar a cikin wani rubutu a shafin   jaridar Washington Post.

shugaban Amurka Joe Biden na ganawa da Faraministan Izraela  Benjamin Netanyahu à ranar 20 ga watan satumba 2023 a birnin New York,
shugaban Amurka Joe Biden na ganawa da Faraministan Izraela Benjamin Netanyahu à ranar 20 ga watan satumba 2023 a birnin New York, AP - Susan Walsh
Talla

Wakilin Radio France Internationale RFI a Miami, David Thomson.Ya ce, shugaban Amuruka ya bukaci mahukumtan isaraela da cewa, su yi duk yadda ya dace wajen kawar dabi’ar cin zarafin falestinawa, ko kuma sabanin  hakan, Amurka a shirye take ta dau wasu jerin matakan ladaftarwa, da suka shafi hana bada Visar shiga kasarta ga masu tsatsauran raáyin yahudawan,  da ke cin zarafin  falestinawa daga mako mai zuwa.

wannan baraza ta  Amuruka na nuna yadda Amuruka ta fara kallon rikicin na Israela da Falestinawa  da idonu irin na adalci,  domin samo hanyoyin kawo karshen mummunar kiyayyar dake tsakaninsu. hakan kuma na nuna  cewa, duk da Amurka  bata fito fili ta bayyana  Izraela a matsayin mai laifi ba, amma ta labe wajen dorawa daidaikun yahudawa yan kakagida laifin cin zarafin Falestinawa, abinda ke nuna cewa,  Amurka ta zama  tabarmar mai nade tabarmar kumya da  hauka ne

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.