Isa ga babban shafi

Shugaba Xi Jinping na kan hanyar sake samun sabon wa’addin shugabancin China

Shugaban kasar Sin Xi Jinping a yau Lahadi ya yaba da manufofin jam'iyyarsa ta kwaminisanci wajen yaki da cutar Covid-19 yayin da yake bude taron shekara biyar na jam’iyyar inda dubban wakilai suka `halara da kuma niyar sake ba shi wa'adi na uku a shugabancin kasar ta China.

Shugaban kasar China Xi Jinping a taron jam'iyya mai mulkin kasar
Shugaban kasar China Xi Jinping a taron jam'iyya mai mulkin kasar © NOEL CELIS / AFP
Talla

A jawabinsa ya yaba da manufofin jam'iyyarsa ta kwaminisanci yayin da yake bude taron shekara biyar na jam’iyyar inda dubban wakilai suka `halara da kuma niyar sake ba shi wa'addi na uku a shugabancin kasar ta China.

A cikin jawabin bude taron da ya dauki tsawon sa’o’I daya da rabi, shugaba Xi ya daukaka da kuma kare tsare-tsare  a karkashin mulkinsa.

Shugaba Xi ya jaddada cewa zai ci gaba da kokarin da jam'iyyar ke yi na kawar da cutar ta Covid, wanda ke kawo cikas ga rayuwar jama'a da kuma kawo cikas ga tattalin arzikin kasar.

Shugaban na China  ya ce yakin da cin hanci da rashawa ya kawar da miyagun dabbi’u a cikin jam'iyyar gurguzu, da sojoji da kuma kasar ga baki daya.

Shugaba Xi ya kuma mayar da hankali kan batutuwan tsaro da ikon mallakar yankunan Hong Kong da kasar China  ke ikirari mallaka  a farkon jawabinsa.

Ya yaba da sauyin da Hong Kong ta yi tare da bin doka da oda.

Ya yi alkawarin da cewa ba zai taba yin watsi da amfani da karfi ba a tsibirin Taiwan mai cin gashin kan sa,al’amarin da ya janyo  cece-kuce.

A cikin jawabi Shugaba Xi  ya fi mayar da hankali kan al'amuran cikin gida, Xi ya shaidawa mahalarta taron cewa, kasar Sin za ta taka rawar gani sosai a harkokin tafiyar da harkokin duniya kan sauyin yanayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.