Isa ga babban shafi

Tedros Adhanom Gebreyesus zai sake jagorantar WHO a wa'adi na 2

Majalisar Lafiya ta Duniya ta sake zaben Tedros Adhanom Gebreyesus ‘dan kasar Habasha a matsayin wanda zai jagoranci Hukumar Lafiya ta Duniya na karin shekaru 5 masu zuwa ba tare da hamayya ba. Kasashen duniya 194 suka kada kuri’ar amincewa da shugabancin Tedros wanda ya fito daga kasar Habasha.

Shugaban hukumar Lafiya na Duniya WHO Tedros Adhanom Gebreyesus.
Shugaban hukumar Lafiya na Duniya WHO Tedros Adhanom Gebreyesus. AFP - JEAN-GUY PYTHON
Talla

Tuni Dr Tedros Adhanom Gebreyesus ya sha rantsuwar kama aiki a wa’adi na biyu na karin shekaru 5 a matsayin shugaban Hukumar Lafiya.

Tedros ya sha alwashin ci gaba da gudanar da aikin sa ba tare da tirsasawar wata kasa ko kuma wasu jama’a ba a matsayin sa na ma’aikacin duniya.

Shugaban ya yi amfani da damar wajen kira ga kasashen duniya da su mayar da zaman lafiya da fahimtar juna a matsayin maganin yaki.

Tedros mai shekaru 57 ya taba rike mukamin ministan lafiyar Habasha da kuma ma’aikatar harkokin waje, kafin nada shi a matsayin shugaban Hukumar Lafiyar ta Duniya WHO.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.