Isa ga babban shafi

Tsohon shugaban Peru da mai dakin sa zasu gurfana a gaban kotu

A kasar Peru,tsohon  Shugaban kasar  Ollanta Humala da mai dakin sa Nadine Heredia za su fuskanci kotu kama daga ranar 21 ga watan Fabrairun shekarar bana bisa laifin samun su da hannu a  batuttuwan da suka jibanci cin hantsi da rashawa.

Tsohon Shugaban kasar Peru tare da mai dakin sa
Tsohon Shugaban kasar Peru tare da mai dakin sa Luka GONZALES AFP/Archivos
Talla

Ana tuhumar wasu mutane 9 da suka hada da mahaifiyar  mai dakin  tsohon Shugaban kasar  da halasta  tareda asasa rashawa da wani kamfanin kasar Brazil yayin yakin neman zaben Shugaban kasar a lokacin..

Wasu daga cikin yan kasar Peru yayin zanga-zangar nuna adawa da Gwamnatin kasar
Wasu daga cikin yan kasar Peru yayin zanga-zangar nuna adawa da Gwamnatin kasar AP - Martin Mejia

Tsohon Shugaban kasar Peru Ollanta Humala mai shekaru 59 ya shugabanci kasar ta Peru  kama daga shekara ta 2011 zuwa 2016 .

Kotu ta umurci a daure tsohon Shugaban kasar shekaru 20 a kurkuku,yayinda ta bukaci a daure mai dakin sa shekaru 26 kurkuku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.