Isa ga babban shafi
Afghanistan

Taliban ta kwace babban birnin lardi na farko a Afganistan

Kungiyar Taliban ta kwace iko da babban birnin lardi na farko a Afghanistan, nasarar farko da ta samu tun bayan kaddamar da farmaki kan dakarun gwamnati, a daidai lokacin da sojojin kasashen waje karkashin jagorancin Amurka suka fara ficewa daga kasar.

Jami'an tsaron sa kai na Afghanistan da sojojin kasar da ke fafatawa da 'yan Taliban, a gundumar Enjil na lardin Herat. Ranar 30 ga Yuli, 2021.
Jami'an tsaron sa kai na Afghanistan da sojojin kasar da ke fafatawa da 'yan Taliban, a gundumar Enjil na lardin Herat. Ranar 30 ga Yuli, 2021. AFP - HOSHANG HASHIMI
Talla

Yayin zantawa da kamfanin dillancin labarai na AFP, Roh Gul Khairzad, mataimakiyar gwamnan Nimroz ta tabbatar da kwace ikon da Taliban tayi da Zaranj, babban birnin lardin.

Mataimakiyar gwamnan ta ce mayakan na Taliban sun karbe iko da birnin na Zaranj da ke kusa da kan iyaka da Iran ne ba tare sun fafata da dakarun gwamnati ba.

Bayanai sun tabbatar da cewa mamayar da Taliban ta yiwa Zaranj babban birnin lardin Nimroz, ta zo ne a daidai lokacin da mayakan kungiyar suka harbe shugaban sashen watsa labarai na gwamnatin Afghanistan a Kabul.

Matakan dai sun sha alwashin ci gaba da kai hari kan manyan jami'an gwamnati domin ramuwar gayya kan hare –haren da sojojin Afghanistan da na Amurka suka kaddamar kansu ta sama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.