Isa ga babban shafi
Masar-Gaza

Masar za ta zuba dala miliyan 500 wajen sake gina Gaza da Isra'ila ta rusa

Gwamnatin Kasar Masar tayi tayin bada agajin Dala miliyan 500 domin sake gina birnin Gaza da hare haren bama baman Israila ya yiwa matukar illa.

Wani yanki na Gaza da Isra'ila da rusa ta hanyar harba bama-bamai da makaman roka.
Wani yanki na Gaza da Isra'ila da rusa ta hanyar harba bama-bamai da makaman roka. REUTERS - Mohammed Salem
Talla

Fadar shugaban kasa AbdelFatah al Sisi ta sanar da gudummawar tare da bayar da gudumawar kwararrun kamfanonin maginan da za suyi aikin.

Tsawon kwanaki Sojin Isra'ila suka shafe suna harba makaman roka baya ga bama-bamai ga yankin na Gaza, wanda ya hallaka tarin fararen hula ciki har da kananan yara, ko da ya ke Isra'lian na ci gaba da ikirarin cewa ta na kaddamar da farmakin ne kan mayakan Hamas.

Wasu Sojin Isra'ila da ke harba makaman roka ga yankin na Gaza.
Wasu Sojin Isra'ila da ke harba makaman roka ga yankin na Gaza. EMMANUEL DUNAND AFP

Masar ta yi ta kokarin ganin ta sasanta Isarila da Falasdinawa domin kawo karshen tashin hankalin da ke gudana a tsakanin su amma abin yaci tura a fadan da ya barke tun ranar 10 ga wannan wata.

Kasar ta kuma aike da tan 65 na magunguna domin taimakawa wadanda suka jikkata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.