Isa ga babban shafi
Syria - IS

Kurdawa sun kame gwamman mayakan IS a Syria

Dakarun sa kai  na Kurdawa a Syria, sun bayyana kame akalla mutane 125 da suke tuhuma da zama mayakan kungiyar IS.

Mayakan Kurdawa a arewacin birnin Aleppo dake kasar Syria.
Mayakan Kurdawa a arewacin birnin Aleppo dake kasar Syria. © Reuters / Khalil Ashawi
Talla

Kurdawan sun kame gwamman mutanen ne, bayan samamen da suka kai kan sansanin ‘yan gudun hijira na Al-Hol dake arewa maso gabashin Syria.

Kakakin mayakan sa kan Kurdawa a karkashin kungiyar SDF Ali al-Hassan, ya ce zarginsu ya yi karfi ne bayan da alkaluma da suka nuna daga farkon shekarar nan zuwa yanzu an yiwa mutane akalla 47 kisan gilla a sansanin na  Al-Hol.

Kurdawan dai sun dade suna zargin cewa akwai mayakan IS dake boye a sansanin mai dauke da ‘yan gudun akalla dubu 62.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.