Isa ga babban shafi
Zaben - Amurka

Mata hudu dake hana Trump sakat a Majalisa sun lashe kujerun su

Fitattun 'Yan Majalisun wakilai mata guda 4 dake adawa da manufofin shugaba Donald Trump a Amurka sun sake lashe kujerun su duk da adawar da shugaban ya dinga musu wajen ganin basu samu nasara ba.

Shugaban Amurka Donald Trump, da mataimakin sa Mike Pence gaban shugabar Majalisar Dokokin kasar Nancy Pelosy
Shugaban Amurka Donald Trump, da mataimakin sa Mike Pence gaban shugabar Majalisar Dokokin kasar Nancy Pelosy REUTERS/Leah Millis
Talla

'Yan Majalisun sun hada da Alexandria Ocasio-Cortez da Ilhan Omar da Rashiad Tlaib da Ayyan Pressley.

Ocasio Cortez ta lashe kujerar ta dake Jihar New York cikin sauki, yayin da kafofin yada labaran Amurka suka sanar da cewar Ilhan Omar ta samu nasara a Minnesota, kamar yadda Ayanna Pressley ta samu a Massachussets da kuma Rashida Tlaib a Michigan.

Ilhan Omar ya bayyana farin cikin ta da sake dawowar kawayen ta a Majalisar wadanda ke takun saka da shugaba Donald Trump.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.