Isa ga babban shafi
China

Kasashe na ci gaba da kauracewa China saboda annobar Corona

Kasashen duniya na ci gaba da kauracewa China ta hanyar dakatar da sufuri tsakaninsu da ita, sakamakon annobar murar mashako ta Corona dake cigaba da halaka rayuka a kasar, da kuma yaduwa zuwa wasu kasashen.

China's isolation grows as virus toll reaches 259. AFP / Anthony WALLACE
China's isolation grows as virus toll reaches 259. AFP / Anthony WALLACE AFP / Anthony WALLACE
Talla

Adadin mutanen da annobar murar ta corona ta halaka a kasar ta China kadai ya kai 259, yayinda kuma annobar ta harbi wasu mutanen akalla dubu 11,791, abinda ya sanya Amurka da Australiada Vietnam dakatar da zirga-zirga tsakaninsu da kasar.

A kasashen ketare kuma kawo yanzu, hukumomin lafiyar Birtaniya, Rasha da kuma Sweden sun tabbatar da bullar annobar murar mashakon ta corona a kasashen, abinda ya kara adadin wadanda annobar ta bazu garesu zuwa akalla kasashe 24.

Ranar Juma'a hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana dokar-ta-baci kan annobar ta Coronavirus wadda ke ci gaba da yaduwa a wasu kasashen duniya.

Shugaban Hukumar Lafiyar ta WHO, Tedros Adhanom Ghebreysus ya ce, babban makasudin ayyana dokar ta bacin kan cutar Coronavirus a duniya, ba wai don abin da ke faruwa a China ba ne, illa don abin da ke faruwa a wasu kasashen duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.