Matar Donald Trump Ta Kammala Ziyara A Afrika
Uwargidan shugaban Amurka Melania Trump na karkare ziyara kasashe hudu na Africa yau lahadi da ziyara kasar Masar.
Wallafawa ranar:
A wani tsokaci da yayi mijin nata Donald Trump ya shaidawa manema labarai cewa matarsa na ziyara kasashen Afrika ne don ta nuna sun damu da jama’a.
Ziyarar Uwargida Melania Trump ya kai ta zuwa kasashen Ghana, Malawi, Kenya sai kuma Masar.
A lokacinda aka tambaye ta yadda take kallon kalaman mijinta a wani lokaci a baya inda yake cewa ‘yan Africa da ‘yan kasar Haiti tamkar wajen kashi yake kallon su, Melania Trump ta ce ita dai bata ji maigidanta ya taba fadin haka ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu