Isa ga babban shafi

Muna da shedar amfani da makami mai guba a Syria-Macron

Shugaban Faransa Emmanuel Macron y ace, yana da sheda kan cewa, gwamnatin Syria ta kaddamar da harin makami mai guba a garin Douma a karshen makon jiya.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron Ludovic Marin/Pool via Reuters
Talla

Shugaba Macron ya ce, nan da wani lokaci zai yanke shawara kan kai wa Syria hari ko kuma a'a.

Tuni dai wasu bayanai suka nuna cewa, kasashen yammaci na shirye-shiryen kai farmaki da makamai masu linzami a matsayin martani kan zargin gwamnatin Bashar Al Assad da amfani da makamin mai guba a Syria.

Sai dai Rasha da ta kasance babbar aminiyar Syria ta fuskan soji, ta gargadi daukan matakan da ka iya tsananta rikici a kasar.

Shugaban Amurka Donbald Trump a shafinsa na Twitter, ya ce, makamai masu linzami na nan a tafe cikin Syria, amma bai sanar da takamammen lokaci harba su ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.