Amuka ta ce yanzu aka fara yakar IS a gabas ta tsakiya
Sakataren Tsaron Amurka Rex Tillerson ya bukaci kasashen da ke kawancen yaki da kungiyar IS da su kara kaimi, inda ya ke cewa murkushe mayakan a filin daga ba wai kawo karshen yakin bane. Tillerson ya bayyana hakan ne a wajen wani taro da suka gudanar a kasar Kuwait.
Wallafawa ranar:
Sakataren tsaron Amurkan ya bukaci kasashen da ke kawance da su a yakin da su ke da kungiyar IS a arewacin Syria , da su kara azama ganin yadda hare haren Turkiyya kan Kurdawa ke kawo musu cikas da koma baya.
Tillarson wanda ke jawabi a taron ministocin tsaron kawancen da ake a Kuwait, ya ce kawo karshen IS a Syriya da Iraqi baya nufin an kawar dasu dun gurungun ba ne akwai sauran aiki gabansu.
Acewar sa, kungiyar IS za ta cigaba da zama babbar barazana a yankin na gabas ta tsakiya, da kuma sauran kasashen Duniya.
Tun cikin watan jiya ne dai Turkiyya ke luguden wuta kan mayakan Kurdawan Syriya da ke samun goyon bayan Amurka, abunda Amurkan ke bayyanawa da matukar komabaya.
A batun hare haren da Saudiyya ke jagoranta kan Yamen kuwa Sakataren tsaron na Amurka ya ce kasar sa za ta yi duk mai yiwuwa don sasanta sabanin, lura da barazanar tsaron da rikicin ya kawo yankin Gulf.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu