Isa ga babban shafi
Jordan-Palestine

Sarkin Jordan zai gana da Abbas kan rikicin Falasdinu

A ranar Litinin mai zuwa ne Sarkin Jordan Abdullah na biyu zai kai ziayarsa ta farko cikin shekaru biyar a birnin Ramallah da ke gabar Yamma da Kogin Jordan, in da zai gana da shugaban Falasdinu Mahmud Abbas.

Sarkin Jordan Abdallah  na biyu
Sarkin Jordan Abdallah na biyu REUTERS/Muhammad Hamed/File Photo
Talla

Wani babban Jami’i a kungiyar Fatah ta Abbas, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP cewa, shugabannin biyu za su zanta kan yadda za a farfado da tattaunawar zaman lafiya tsakanin Isra’ila da Falasdinu.

Tun a shekarar 2014 ne, tattaunawa tsakanin bangariorin biyu ta tsaya cak.

Kasar Jordan ta soma baki a cikin watan jiya don samar da masalaha kan rikicin da ya barke tsakanin jami’an tsaron Isra’ila da Falasdinawa a harabar Masallacin Haram al-Sharif da ke tsohon birnin Kudus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.