Isa ga babban shafi
Saudiya

Saudiya ta umurci ‘Yan kasar da su gujewa tarurruka a Jordan

Hukumomi a kasar Saudia sun umurci ‘Yan kasar da su gujewa halarta tarurruka da Jami’oi a yayin da bore akan tsadar mai ya yi sanadiyar mutuwar mutum daya, ya kuma raunata mutane 71 a kasar ta Jordan. 

Sarki Abdallah na kasar Saudiya (Hagu)
Sarki Abdallah na kasar Saudiya (Hagu) REUTERS
Talla

Ofishin Jakadancin kasar ne a Amman ya fitar da wannan sanarwa ga masu aiki a kasar ta Jordan da dalibai dake karatu a kasar.

Tashin hankali a kasar ta Jordan ya barke ne a ranar Talata bayan karin farashin gas da aka yi a kasar da kashi 53 da kuma na mai da kashi 12.

A cewar Firaministan kasar Jordan, Abdulla Nsur, karin ya zama dole domin kasar na bukatar ta tsohe gibin kasafin kudin bana na kudi Dalar Amurka biliyan 3.5. da aka samu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.