Isa ga babban shafi
Jamus-Amurka

Jamus ta zargi Trump da kitsa rikicin Larabawa

Kasar Jamus ta zargi shugaban Amurka Donald Trump da kitsa rikici tsakanin kasashen Larabawa domin ganin an samu cinikin makamai.

Shugaban Amurka Donald Trump tare da Sarki Salman na Saudiya
Shugaban Amurka Donald Trump tare da Sarki Salman na Saudiya MANDEL NGAN / AFP
Talla

Ministan Harkokin Wajen Jamus Sigmar Gabriel ya ce, kwangilar makaman da Saudiya ta bai wa Amurka na daga cikin dalilan da suka haifar da rikicin da aka samu tsakanin Saudiyar da kawayenta musamman kasar Qatar

Gabriel ya ce, ya na fargabar abin da zai biyo baya sakamakon wannan matsalar da aka samu a fadin yankin  kasashen Larabawa baki daya.

A farkon makon ne kasashen Saudiya da Masar da Yemen da Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrai suka katse hulda da Qatar tare da rufe kan iyakokinsu na sama da na ruwa da na kasa da Qatar.

Daukan wannan mataki na zuwa bayan sun zargi Qatar da tallafa wa kungiyoyin 'yan ta'adda, zargin da ta musanta.

Shugaba Donald Trump ya ce, ziyarar da ya kai Saudiya ce ta haifar da matakin da aka dauka kan kasar Qatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.