Isa ga babban shafi
Qatar

Kuwaiti zata warware rikicin Qatar da sauran kasashen Larabawa

Sarkin kasar Kuweiti Sheikh Sabah al-Ahmad Al-Sabah ya isa birnin Riyad na Saudiyya, domin shiga tsakani da nufin shawo kan rikicin diflomasiyyar da ya barke tsakanin wasu kasashen Larabawa da kuma Qatar.

Sarkin kasar Qatar Tamim Ben Hamad Al-Thani
Sarkin kasar Qatar Tamim Ben Hamad Al-Thani Reuters
Talla

Rikicin da ya sanya kasashen da suka hada da Hadaddiyar daular Larabawa, Masar, Baharain, Libya, Yemen, Maldives a karkashin jagorancin Saudiyya suka yanke alaka tsakaninsu da kasar ta Qatar.

Daga cikin matakan da suka dauka dai akwai dakatar da zirga-zirgar jiragen sama tsakaninsu da ita, sai kuma rufe iyakar da ke tsakanin Qatar din da Saudiyya.

Tuni dai ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohamed Bin Abdul Rahman, ya ce kasar a shirye take, ta shiga tattaunawar sulhu da sauran kasashen domin warware sabanin da ke tsakaninsu, inda y ce Qatar ba ta da niyyar daukar wani mataki na ramuwar gayya akansu domin zai shafi rayuwar al’ummomin kasashen da ke cikin kungiyar hulda da juna a yankin Gulf baki daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.