Wani jigo a kungiyar Taliban ya rasu
Wani harin sojin Amurka ya yi sanadiyyar mutuwar daya daga cikin manyan kwamandojin Taliban a kasar Afghanistan.Rundunar Sojin Amurka na taka rawa a yakin kasar Afghanistan.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun tabbatar da mutuwar Mullah Abdul Salam Ahkund wanda ke kiran kansa gwamnan Lardin Kunduz bayan wani hari da ake jin cewa sojojin Amurka ne suka kai shi.
Amurka na daga cikin kasashen dake kokarin sake dawowa da zaman lafiya a kasar ta Afghanistan ,kasar da aka share tsawon shekaru ana tafka fada tsakanin kabilu.
Ya zuwa yanzu kungiyar ta Taliban ba ta ce upon ba kan mutuwar Mullah Salam Ahkund.
A watan Janairu shekarar 2017 ne Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar da gidauniyar neman agaji Dala miliyan 550 domin taimakawa Afghanistan, wanda kashi 1 cikin 3 na al’ummar kasar ke cikin halin na tagayara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu