Shugabanni Afrika sun ta ya Trump murna
Shugabannin Kasashen Afrika na ci gaba da aike sakon ta ya murna ga Donald trump sakamakon nasarar da ya samu, da kuma fatar yin aiki tare.
Wallafawa ranar:
Cikin shugabannin da suka bayyana sakwannin nasu sun hada da Uhuru Kenyatta na Kenya, da Jacob Zuma na Afirka ta kudu da Muhammadu Buhari na Najeriya.
Shi kuma Shugaban Masar Abel Fata al-sisi fatan ganin sabon shugaban Amurkan ya taka rawar dawo da zaman lafiya a gabas ta tsakiya ya yi, bayan taya shi murna, a daidai lokacin da Shugaban Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana Trump a matsayin abokin tafiya na gaskiya wajen sake karfafa Isra’ila.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu