Isa ga babban shafi
Turkiya-Jamus

Jamus ta shashantar da kiran jakadanta a Turkiya

Gwamnatin Jamus ta shashantar da matakin da Turkiya ta dauka na kiran jakadanta bayan gangamin da magoya bayan shugaba Erdogan suka yi a birnin Cologne .

Magoya bayan shugaban Turkiya kimanin dubu 30 sun gudanar da gangami a birnin Cologne na Jamus
Magoya bayan shugaban Turkiya kimanin dubu 30 sun gudanar da gangami a birnin Cologne na Jamus REUTERS/Thilo Schmuelgen
Talla

Mai magana da yawun ministan harkokin wajen Jamus, Martin Schaefer ya ce, kiran jakadanta da Turkiya ta yi ba wani muhimmin abu bane, lura da cewa an saba ganin haka tsakanin kasashe biyu da ke huldar diflomasiya.

Sai dai Schaefer ya tabbatar wa manema labarai cewa, kiran nada nasaba da gangamin da magobayan Erdowan din suka yi a jiya.

An dai gudanar da gangamin ne don nuna goyon baya ga Erdogan saboda yunkrin juyin mulkin da aka yi masa a ranar 15 ga watan jiya duk da cewa juyin mulkin bai yi nasara ba.

Kimanin Turkawa miliyan uku ne ke zaune a Jamus, kuma ita ce kasar waje da Turkawan suka fi yawa a ciki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.