Isa ga babban shafi
saudiya

An kama wadanda suka kitsa harin Madina

Hukumomin Saudiya sun cafke mutane 19 da ake zargi da hannu a hare-haren ta’addancin da aka kai wa kasar a ranar Litinin da suka hada da wanda aka kai kusa da masallacin Annabi da ke birnin Madina.

Wani dan asalin kasar Saudiya ne ya kai hari a birnin Madina mai dauke da kabarin Manzan Allah S.A.W
Wani dan asalin kasar Saudiya ne ya kai hari a birnin Madina mai dauke da kabarin Manzan Allah S.A.W REUTERS
Talla

An kama mutane 12 ‘yan asalin kasar Pakistan da kuma mutane 7 ‘yan asalin kasar ta Saudiya yayin da aka bayyana wani matashi mai shakaru 26 a matsayin wanda ya kai harin Madina.

Matashin mai suna Naer Muslim Hamad, dan asalin Saudiya ne kuma rahotanni sun ce, mai mu’amala da miyagun kwayoyi ne.

Harin na Madina shi yafi tayar da hankulan kasashen musulmi na duniya, lura da matsayin birnin wanda ke dauke da kabarin Annabi Muhammadu tsira da amincin Alla su kara tabbata a gare shi.

Masharta dai na ganin cewa kungiyar IS mai da’awar kafa daular Islama, ita ce ta shirya hare haren da aka kai Madina da Jedda da kuma Qatif duk a rana guda.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.