Isa ga babban shafi
G7-Rasha

Ba mu da niyyar janyewa Rasha takukumai-G7

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce kasashe 7 masu karfin tattalin arziki a duniya ba su da niyyar janyewa takunkuman da suka kakaba wa kasar Rasha a lokacin wannan taro nasu.

Shugabanni Kasashe bakwai, masu karfin tattalin arziki a duniya
Shugabanni Kasashe bakwai, masu karfin tattalin arziki a duniya 路透社
Talla

Merkel ta ce batun cire wa kasar takunkumai sakamakon rawar da take takawa domin wargaza kasar Ukraine wadda babbar aminiya ce ga kasashen 7, sam ba ya cikin abubuwan da suke tattaunawa a kai.

Takukuman karayar tattalin arziki da aka kakkabawa Rasha na cigaba da tasiri ga cigaban tattalin arzikin kasar.

A ranar Alhamis ne Shugaban Kungiyar kasashen Turai Donald Tusk ke bayyana ra'ayinsa kan wannan batu, da yake gani lokaci yayi da za a dai-dai al'amura tsakanin Rasha da Ukraine da kuma batun rikicin tekun kasar China.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.