Isa ga babban shafi
Brazil

A na tuhumar tsohon shugaban kasar Brazil

Masu gabatar da kara a Brazil sun shigar da kara inda su ke tuhumar tsohon shugaban kasar Inacio Lula da Silva da laifin halarta kudaden haram, a wani yunkuri da ake ganin na iya kifar da gwamnatin kasar da ya taimaka wajen dora ta kan karagar mulki.

Tsohon shugaban kasar Brazil, Inacio Lula da Silva
Tsohon shugaban kasar Brazil, Inacio Lula da Silva REUTERS/Paulo Whitaker
Talla

Ofishin mai gabatar da kara ya ce, tsohon shugaban da ya yi suna wajen farfado da tattalin arzikin Brazil da kuma sanya ta cikin kasashen da arzikinsu ke saurin habbaka, ya boye wani gidan alatu da ya mallaka a bakin tekun Sao Paolo da kuma wani a Guaruja wanda hakan babban laifi ne.

An dade ana zargin gwamnati mai ci ta shugaba Dilma Roussefff wadda tsohuwar babbar hafsa ce a ofishin Lula da cin hanci da kuma halarta kudaden haramun.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.