Amurka-Najeriya
Boko Haram: Amurka za ta horar da sojin Najeriya
Kasar Amurka na nazarin aiko da tawagar kwararru domin bai wa sojojin Najeriya horo na musamman wadanda ke fada da mayakan Boko Haram a Arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani jami’in tsaron Amurka ne ya bayyana haka inda ya ce, Amurka za ta taimaka wa Najeriya bayan shugaba Muhammadu Buhari ya nemi tamakon hukumomin Washington.
Kuma daga cikin bukatun shugaba Buhari ga Amurka sun hada da aikawa da kwararru domin horar da dakarun na Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu