Isa ga babban shafi
Syria

‘Yan adawa za su kauracewa taron Syria a Geneva

Kungiyar ‘Yan adawar Syria ta jaddada matsayinta na kauracewa taron sasanta rikicin kasar da Majalisar Dinkin Duniya ta sanar za a soma a yau Juma’a a Geneva.

Mai shiga tsakanin rikicin Syria na Majalisar Dinkin Duniya de Mistura
Mai shiga tsakanin rikicin Syria na Majalisar Dinkin Duniya de Mistura Reuters
Talla

‘Yan adawar sun ce za su kauracewa zaman taron har sai an amince da bukatunsu na shigar da kayan jin-kai a yankunan da ke cikin matsananci hali na yunwa.

‘Yan adawar wadanda Saudiya ke marawa baya sun ce sai idan an cim ma yarjejeniyar shigar kayan jin kai sannan za su halarci taron sasanta rikicin na Syria.

Matakin kauracewa taron na ‘Yan adawar ya haifar da fargaba akan nasarar  kokarin kawo karshen yakin da aka kwashe shekaru 5 ana fafatawa a Syria.

Sama da mutane 260,000 suka mutu a rikicin Syria, kuma jekadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Steffan de Mistura yana ganin wannan dama ce ta kawo karshe zubar da jini a kasar.

‘Yan adawar na son dakarun gwamnatin Bashar Al Assad su dakatar kai hari tare da bayar da izinin shigar da kayan jinkai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.