Isa ga babban shafi
Afghanistan

Hukumomi a Afghanistan Sun ce Mutane 51 Suka Mutu a Hare-Haren Bama-Bamai na Juma'a

Hukumomi a kasar Afghanistan sun gaskata cewa mutane 51 ne suka mutu bayan kazaman hare-haren bama-bamai ranar Juma'a a birnin Kabul mafi muni tun bayan ficewar dakarun kawance na hadin guiwa na NATO a watan 12 da ya gabata. 

'Yan Sanda na jigilan gawarwakin wasu daga cikin mamata
'Yan Sanda na jigilan gawarwakin wasu daga cikin mamata REUTERS/Ahmad Masood
Talla

Harin na jiya ya lalata gine-gine da yawa da jikkata daruruwan mutane.

Asibitoci sun cika sun batse da mutane da suka sami raunuka yayin hare-haren mafiya muni tun bayan sanar da mutuwar Shugaban Taliban Mullah Omar.

Hare-haren na kara nuna rashin tabbacin ingantaccen tsaro a wannan kasa da yaki ya lalata.

Harin farko cikin dare ranar Juma'a a tsakiyar birnin Kabul mutane 15 suka mutu nan take , yayinda wasu 250 suka jikkata.

Daga bisani kuma aka sake samu wani hari a harabar inda ake daukan kuratan 'yan sanda inda nan take kurata da wasu fararen hula 27 suka mutu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.