Isa ga babban shafi
Afghanistan

Taliban ta kai harin farko a Afghanistan bayan mutuwar shugabanta

Kungiyar Taliban ta hallaka mutane 6 a harin farko da ta kai Cibiyar jami’an tsaro a Afghanistan bayan sauyin shugabancin da aka samu a kungiyar sakamakon rasuwar Mullah Omar.

Mayakan Taliban sun shafe shekaru suna yaki a Afghanistan
Mayakan Taliban sun shafe shekaru suna yaki a Afghanistan AFP PHOTO / Noorullah Shirzada
Talla

Mataimakin jami’in Yan Sandan Afghanistan da ke Yankin Logar Muhammad Qari Wara ya ce wata motar tankin ruwa shake da bama bamai ne ta fashe inda ta kashe fararen hula uku da jami’an tsaro uku.

Ma’aikatar cikin gidan kasar ta tabbatar da harin wanda shi ne na farko da Mayakan Taliban suka yi ikirarin kai wa tun bayan mutuwar shugabansu Mullah Umar.

A ranar Juma’a ne Taliban ta sanar da nada Mullah Akhtar Mansour a matsayin sabon shugaba.

A cikin makon nan ne wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa an samu karuwar mutuwar fararen hula a kasar Afghanistan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.