Isa ga babban shafi
IRAN-Nukiliyya

Yarjejeniyar Shirin Nukiliyar Iran na gab da Nasara

Ministan harkokin wajen Iran Muhammad Javad Zarif, ya shaida cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar da ake yi game da shirin nukiliyar kasar a birnin Vienna. To sai dai akwai bukatar sadaukarwa daga kowane bangare kafin cimma yarjejena kan wannan batu.

Kasashen dake tattauna shirin Nukiliya Iran
Kasashen dake tattauna shirin Nukiliya Iran ISNA
Talla

Javad Zarif ya ce akwai sauran ‘yan bambance-bambancen da suka rage a tsakaninsu, sai dai kuma yana ganin cewa ba su taba kusantar matsayi na fahimtar juna kamar yadda sukayi a jiya ba, to amma duk da haka ba shi da tabbas, saboda kafin cimma yarjejeniya, akwai bukatar sadaukarwa daga kowane bangare.

Ya kuma bayyana yadda wasu da farko suka bukaci yin amfani da karfin soja da takunkumai na tattalin arziki domin tursasawa Iran, amma daga karshen suka rungumi hanyar tattaunawa, to amma duk da haka, a akwai bukatar yin wani abu da za a bayyana shi a matsayin tarihi, ina nufin cimma yarjejeniya a cewar Ministan.

Iran dai na cewa anata bangare ta shirye domin kulla yarjejeniyar da babu kwaruwa a cikinta, domin buda sabon babi da nufin fuskantar muhimman kalubale da ke gabansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.