Faransa zata bayar da tallafin kudi don Ebola
Kasar Faransa tace zata bayar da gudummawar euro miliyan 20 don yaki da cutar Ebola a Nahiyar Afrika, tare da kuma bude wasu cibiyoyin kula da lafiya. Shugaba Francois Hollande ya sanar da shirin wanda ya kunshi gina asibiti mai cin gadaje 200 a kasar Guinea.
Wallafawa ranar:
Jami’in kula da yaki da cutar ebola a kasar Jean-Francosi Delfraissy yace nan da kwanaki 10 Faransa zata fitar da kudin.
Tuni dai Shugaban Amurka da kungiyar agaji ta Red Cross suka ce ana samun nasara a yakin da ake yi da Ebola a kasashen duniya.
Hukumar lafiya ta duniya tace a cikin makon nan ne zata fara gwajin rigakafin cutar Ebola a kasar Switzerland.
WHO tace kafin karshen shekara ta 2015 za’a samu wadatuwar dubban rigakafin cutar Ebola mai yin kisa cikin hanzari a kasashen yammacin Afrika. Hukumar tace za’a samar da rigakafin ne kusan Miliyan guda.
Wannan na zuwa ne a yayin da shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Turai suka amince da tallafin kudi sama da euro Biliyan guda domin yaki da cutar Ebola a kasashen Afrika.
Mutane kusan 5,000 suka mutu a kasashen Guinea da Liberia da Saliyo saboda Ebola, kuma masana yanzu sun bayyana fargaba akan barazanar yaduwar Cutar Ebola a kasashen yammacin Afrika.
A cikin makon nan ne aka samu bullar Cutar Ebola a Mali bayan cutar ta bulla a Najeriya.
Kimanin mutane 43 ne ake lura da lafiyarsu a Mali wadanda suka yi mu’amula da wata yarinya ‘Yar shekaru biyu da ta yi sanadin bullar cutar Ebola a cikin kasar daga Guinea.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu