Isa ga babban shafi
Masar

Isra’ila da Hamas sun koma teburin sulhu

Wakilan Isra’ila da Hamas sun soma tattaunawa a kasar Masar domin cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta mai dorewa, kafin wa’adin ta wuccin gadi ya cika, da nufin kawo karshen zubar da jini a Gaza.

Sojan Isra'ila yana harba wa Falasdinawa masu zanga zanga hayaki mai sa hawaye a gabar yamma da kogin Jordan
Sojan Isra'ila yana harba wa Falasdinawa masu zanga zanga hayaki mai sa hawaye a gabar yamma da kogin Jordan REUTERS/Mohamad Torokman
Talla

Kusan Falasdinawa 2,000 Isra’ila ta kashe sama da wata guda tana kai farmaki a Gaza

Kasar Masar da ke jagorantar zaman tattautawar, tana fatar bangarorin biyu zasu amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta.

Kodayake wakilan Hamas suna da bukatu da suke son dole sai Isra’ila ta amince kafin su amince da yarjejeniyar, musamman bukatar neman a kawo karshen killacewar da Isra’ila ta yi wa zirin Gaza tsawon shekaru bakwai.

Isra’ila kuma tana da bukatu na tsaro da ta ke son Hamas ta amince kafin kulla sabuwar yarjejeniyar ta tsagaita wuta.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.