Isa ga babban shafi
Colombia

Gwamnatin Colombia ta kulla yarjejeniya da 'yan tawayen FARC

Gwamnatin Kasar Colombia ta kulla yarjejeniya da Yan Tawayen FARC wanda zai basu damar shiga harkokin siyasa muddin suka kawo karshen daukar makaman da suka kwashe shekaru 50 suna yi.Wani jami’in diflomasiyar kasar Cuba dake shiga tsakanin tattaunawar da ake a birnin Havana, Rodlfo Benitez, yace sun cimma matsaya kan daya daga cikin manyan batutuwan da bangarorin suke takaddama akai.Yanzu abinda ya rage, shine batun safarar hodar ibilis, biyan diyya da kuma aje makamai.  

Ministan Tsaron kasar Colombiya, Juan Carlos Pinzon yana duba makaman da aka karbe daga wajen 'yan tawayen FARC
Ministan Tsaron kasar Colombiya, Juan Carlos Pinzon yana duba makaman da aka karbe daga wajen 'yan tawayen FARC REUTERS/Filiberto Guarnizo-Defense Ministry/Handout via Reuters
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.