Amurka-Gabar ta tsakiya
Amnesty ta zargi Amurka da aikata laifukan yaki
Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama ta Amnesty International, tace harin da Amurka take kaiwa da jiragen dake sarrafa kansu a kasashen Pakistan da Yemen sun saba ka’ida kuma ana iya tuhumar kasar da laifufukan yaki.Kungiyar tace, ta gudanar da bincike kan wasu hare hare guda 9 da Amurka ta kai Arewacin Waziristan, wanda ya tabbatar mata cewar mutanen da aka kaiwa harin basa dauke da makamai.Wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar a Pakistan, yace Amurka ta kashe fararen hula sama da 400 a irin wadanan hare hare.
Wallafawa ranar: