Isa ga babban shafi
Iraqi-Amurka

Gwamnatin Iraqi ta kama hanyar rugujewa inji Biden

Mataimakin Shugaban kasar Amuka, Joe Biden, yace Gwamnatin kasar Iraqi, ta kama hanyar rugejewa, sakamakon barakarar da aka samu tsakanin Fira Minista Nuri al Maliki mabiyin Shia, da Mataimakin shugaban kasa, Tariq al Hashemi, mabiyin Sunni.

Mataimakin Shugaban kasar Amurka Joe Biden yana ganawa da  Jalal Talabani  na Iraqi a Bagdad
Mataimakin Shugaban kasar Amurka Joe Biden yana ganawa da Jalal Talabani na Iraqi a Bagdad REUTERS/Saad Shalash
Talla

Biden yace rashin taka tsan-tsan tsakanin bangarorin biyu, na iya haifar da tashin hankali a kasar, kamar yadda aka samu a shekarar 2006-2007 inda aka kashe dubban mutane.

Yanzu haka Hashemi ya samu mafaka a Yankin Kurdistan mai cin gashin kansa, bayan umurnin kama shi da Fira Ministan ya bayar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.