Isa ga babban shafi

Adadin wadanda suka mutu sakamakon gobarar Hawaii ya kai 93

A kalla mutane 93 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon gobarar dajin da ta mamaye kauyen Maui, dake kan tsibirin Hawai na kasar Amurka, kamar yadda sabon sakamakon iftila’in ya nuna.

Wani mutum kenan yake tafiya cikin motocin da suka kone sakamakon gibarar Hawaii.
Wani mutum kenan yake tafiya cikin motocin da suka kone sakamakon gibarar Hawaii. AP - Rick Bowmer
Talla

A ranar Asabar, mazauna yankin Maui, sun bayyana Iftila’in da zama mafi muni a kan manda  ya taba faruwa a yankin kasar Amruka, inda tsibirin na Hawai ya fuskanci ambaliyar tsunami, da  ta yi sanadiyar mutuwar mutane 61 a 1960

Yanzu haka dai bayan lafawar wutar,  mazauna garin Lahaina,  mai kunshe da kimanin mutane dubu 13.000  sun fara nazarta  irin barnar da wutar dajin  ta yi masu, inda ta  barsu hannu rabbana,  ba komai sai rayukansu.

Anthony Garcia, wani tsoho ne mai shekaru  80 a duniya, ya bayyana matukar damuwarsa,  bayan ya rasa komai,  a garin da ya tare yau sama da shekaru 30 da suka gabata.

Mutanen da suka tsira da rayukansu daga iftila’in na ci gaba da bincikar gawawakin da wutar ta lakume,  bisa zummar samun hotunansu

Duk inda ka duba,  gabarar ta lashe gidaje da gonaki musaman a katafaren  dajin gonakin ayaba, da ke jawo masu yawon buda ido, wadanda  yanzu haka gobarar ta lashe, kamar ba a taba yin su ba.

Kamar dai mazauna tsibirin, yanzu haka kotu ta bayyana buda soma binciken shara’a, domin  gano dalilin da ya sa wutar ta yi kamarin, binciken da ya karkata kan yadda mahukumta suka  gudanar da  ayukan agajin gaggawa a lokacin gobarar. Yadda ayukan sadarwa suka gudana a lokacin iftila’in na daga cikin abubuwan da ake dora almar tambaya a Kansu.

Mazauna yankin sun sanar da AFP cewa, sun yi amfani ne da tsohuwar hanyar sadarwa,  daga wannan ita ciyar kwakwa zuwa wacan, ma’ana daga baki zuwa kunne.

 

Uwargida Vilma Reed, ta bayyana cewa, ita bata hangi wutarba sai bayan da ta zo daf da kofar gidanta da wutar ta lakume.

Garin Maui dai, ya fuskanci katsewar wutar lantarki a lokacin gobarar, wanda ya sa  lambar  layin wayar gaggawa 911 ta daina aiki a wasu yankuna na Tsibirin, a yayin da  kuma aka ce, ba a kunna jiniyar gargadin tashin gobara ba a lokacin  faruwar iftila’in.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.