Isa ga babban shafi

ECOWAS ta bukaci maido da tsohon jadawalin zaben kasar Senegal

Kungiyar ECOWAS, ta bukaci gwamnatin Senegal ta gaggauta maido da tsohon jadawalin zaben shugabancin kasar da ta sauya, bayan da ta dage gudanarsa daga watan Fabarairu zuwa karshen wannan shekara.

Wasu masu zanga-zanga yayin boren adawa da matakin dage zaben shugabancin kasar Senegal daga wtan Fabarairu zuwa karshen shekarar 2024.
Wasu masu zanga-zanga yayin boren adawa da matakin dage zaben shugabancin kasar Senegal daga wtan Fabarairu zuwa karshen shekarar 2024. © AFP - SEYLLOU
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar, kungiyar kasashen ta yammacin Afrika ta ce tana bin dukkanin abubuwan da ke faruwa a Senegal sau da kafa, bayan zanga-zangar adawar da ta rikide zuwa tarzoma saboda dage babban zaben da aka tsara yi daga ranar 25 ga watan Fabrairu zuwa 15 ga watan Disamba.

A daren ranar Litinin, Majalisar dokokin kasar Senegal ta kada kuri'ar tabbatar da daukar matakin, tare da bai wa  shugaba Macky Sall damar ci gaba da zama kan karagar mulki har sai an nada wanda zai gaje shi.

Wannan ce ta sa a jiya Talata ‘yan adawa suka kamanta dage zaben shugabancin na Senegal da juyin mulki, rashin tabbatas din da suka ce shi ne mafi muni da al’ummar kasar suka gani a siyasance cikin gwamman shekaru.

Senegal dai ba ta taba fuskantar juyin mulki ba tun bayan samun 'yancin kai daga Faransa a shekara ta 1960, abinda ya sa ake mata kallon zama abin misali a bin tsarin mulkin dimokaradiya. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.