Isa ga babban shafi

Amurka ta dakatar da baiwa Gabon tallafin kudade

Gwamnatin Amurka ta dakatar da da baiwa Gabon duk wasu tallafin kudade, a ci gaba da daukar mataki kan sojojin kasar da suka yi juyin mulki a watan da ya gabata.

Sakataren harkokin wajen Amurka Antoni Blinken
Sakataren harkokin wajen Amurka Antoni Blinken © RFI
Talla

Sakataren harkokin wajen Amurka Antoni Blinken wanda ke bayar da wannan sanarwa, ya ce babu wani dalili da zai sa Amurka ta ci gaba a baiwa kasar tallafin kudade karkashin gwamnatin soji.

Sai dai sanarwar ta Antoni Blinken ba ta fayyace fannonin da za a dakatar da baiwa kudin ko kuma adadin kudin da za a daina bayarwa ba.

Gabon ita ce kasa ta biyu da aka yi juyin mulki a nahiyar Afrika cikin watanni biyu kachal.

Dakatar da bai wa kasashen da aka yi juyin mulki tallafin kudade ba wani sabon abu bane a Amurka, wadda ke zama tamkar madubin dubawar kasahen da ke takama da dimokradiyya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.