Isa ga babban shafi

Tawagar Turai da ke sa ido a zaben Zimbabwe ta musanta labarin zargin hannu a badakalar rashawa

Tawagar Tarayyar Turai da ke sa ido kan zabukan kasar Zimbabwe a yau Asabar ta musanta labarin da wata jarida mallakar gwamnatin kasar ta wallafa na zargin cewa suna da hannu a badakalar cin hanci.

Magoya bayan 'yan siyasa a kasar Zimbabwe
Magoya bayan 'yan siyasa a kasar Zimbabwe AFP
Talla

A ranar 23 ga watan Agusta za a gudanar da zabukan  shugaban kasa, 'yan majalisa da wakilan kananan hukumomi.

 Jaridar The Herald daily a kasar ta Zimbabwe a ranar Juma'a ta ruwaito cewa wata tawagar kafofin yada labarai ta Tarayyar Turai ta gana da 'yan jarida 18 tare da raba  barasa da kayan abinci da nufin 'yan jarida su yi ikirarin wuce gona da iri ga tsarin zaben da ya gudana a wannan kasa.

Shugaban kasar Zimbabwe kuma dan takara Emmerson Mnangagwa mai shekaru 80
Shugaban kasar Zimbabwe kuma dan takara Emmerson Mnangagwa mai shekaru 80 AP - Tsvangirayi Mukwazhi

Sai dai shugaban tawagar ta Turai Fabio Massimo Castaldo da yake ambato wasu majiyoyi da ba a bayyana sunayensu ya yi mamakin irin zarge-zargen batanci da aka buga a cikin kafofin yada labaran Zimbabwe, ya na mai bayyana cewa “Wadannan zarge-zargen sun samo asali ne daga jita-jita da ba su da tushe, kuma kage ne gaba daya.”

Shugaba Emmerson Mnangagwa, da jagoran 'yan adawa Nelson Chamisa,
Shugaba Emmerson Mnangagwa, da jagoran 'yan adawa Nelson Chamisa, AFP/File

 Ya bayyana yunƙurin da aka yi a baya na bata sunan manufar wannan tawaga, ya kuma ƙarasa da cewa irin waɗannan labaran ba su dace ba a wannan lokaci da ake fatan cimma zaman lafiya mai dorewa a wannan kasa ta Zimbabwe, da kuma ganin kokarin da kungiyar Tarrayar Turai ke yi ta fuskar kawo nata kokari domin tabbatar da sahihancin wannan zabe.

Dan adawa ga shugaban kasar Zimbabwe  Nelson Chamisa
Dan adawa ga shugaban kasar Zimbabwe Nelson Chamisa AFP/File

Sauran wadanda suka kasance ‘yan sanya ido a zaben sun hada da kungiyar Tarayyar Afirka, da Commonwealth da kuma kungiyar raya kasashen kudancin Afirka (SADC). 'Yan takara 12 ne dai suka fafata a zaben shugaban kasa, zaben da ake kyautata zaton Shugaba mai ci Emmerson Mnangagwa mai shekaru 80 da Nelson Chamisa mai shekaru 45 su kasance a zagaye nag aba har idan ta kama a wannan kasa  da ke fama da matsalar cin hanci da rashawa da hauhawar farashin kayayyaki da fatara da kuma rashin aikin yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.