Isa ga babban shafi

MDD ta tsawaita takunkumin haramta cinikin makamai da Sudan ta Kudu

Kwamitin Sulhu na majalisar dinkin duniya ya kada kuri'ar tsawaita takunkumin hana sai da wa Sudan ta Kudu makamai gami da takunkuman da aka lafta wa wasu daidaikun mutane a kasar.

Dakarun Sudan ta Kudu rike da Makamai suna iho a sansaninsu da ke yankin Bentiu
Dakarun Sudan ta Kudu rike da Makamai suna iho a sansaninsu da ke yankin Bentiu REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

A shekarar 2011 Sudan ta Kudu ta zama kasa mai cin gashin kanta bayan ballaewa daga Sudan, sai dai bayan shekaru biyu kasar ta fada cikin rikicin da ya tagayyara   miliyoyin mutane.

Kididdiga ta nuna cewar a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2018, mutane 400,000 aka kiyasta sun mutu yayin da wasu miliyoyi suka rasa matsugunansu, sakamakon yakin basasar da ya barke tsakanin sojoji masu biyayya ga shugaba Salva Kiir da kuma tsagin dakarun da goyon bayan mataimakinsa Riek Machar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.