Isa ga babban shafi

An cigaba da barin wuta a Sudan duk da tsagaita wutar kwanaki 3

Rahotanni daga Sudan na cewa an jiyo amon harbe-harbe da manyan bindigogi a Khartoum da kuma Omdurman birni na biyu mafi girma a kasar.

Hayaki na tashi a kusa da babban asibitin kasa da kasa na Doha da ke Kharoum babban birnin kasar Sudan.
Hayaki na tashi a kusa da babban asibitin kasa da kasa na Doha da ke Kharoum babban birnin kasar Sudan. AP
Talla

Sabon fadan ya barke ne duk da sabuwar yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta tsawon sa'o'i 72 da Amurka jagoranci kullawa tsakanin sojojin Sudan da dakarun musamman na kai daukin gaggawa RSF, masu biyayya ga mataimakin shugaban Sudan Muhammed Hamdan Daglo.

A birnin Geneina da ke yammacin yankin Darfur, ma wani fadan ne ya barke a Talatar nan kamar yadda sahihan majiyoyi daga Sudan din suka bayyana.

Tuni Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da dakatar da  ayyukan jin kai a wasu sassan kasar, saboda kazancewar da rikicin kasar  ke yi, wanda ya  barke tun a ranar  15  ga  watan nan na Afrilu.

Akalla mutane 427 aka tabbatar da mutuwarsu a rikicin na Sudan, yayin da wasu kusan dubu 4 suka  jikkata.

Kawo yanzu kuma dubun dubatar baki ‘yan kasashen ketare da ma ‘yan kasar ta Sudan aka kwashe daga kasar zuwa kasashen Masar, Sudan ta Kudu da kuma Chadi cikin ‘yan kwanakin da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.