Tsohon shugaban Zambia Kenneth Kaunda ya mutu yana da shekaru 97
Tsohon shugaban kasar Zambia Kenneth Kaunda ya mutu yau ya na da shekaru 97 bayan fama da cutar toshewar hanyoyin lumfashi da ta kai shi ga kwanciya a asibiti na ‘yan kwanaki.
Wallafawa ranar:
Kaunda shugaba mafi dadewa a kujerar mulkin kasar Zambia, ya shafe shekaru 27 yana jan ragamar kasar tun bayan samun ‘yancin kai daga birtaniya a 1964 gabanin tsarin demokradiyya ya yi awon gaba da kujerarsa.
Kaunda wanda ya yi gwagwarmayar kalubalantar turawan mulkin mallaka ana kallonsa a matsayin jajirtaccen jagora ba kadai ga kasar sa ta Zambia ba harma da nahiyar Afrika baki daya.
A litinin din da ta gabata ne aka garzaya da Kaunda asibiti bayan tsanantar cutar ta sa yayinda rai ya halinsa a yau litinin.
Kenneth Kaunda shi ne shugaban farko da Nelson Mandela ya ziyarta a shekarar 1990 bayan fitowa daga kurkuku, yayinda ya ke matsayin na karshe a jerin jagororin Afrika da suka yi gwagwarmayar neman 'yanci daga turawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu