Isa ga babban shafi
Eritrea - Tigray

Eritrea ta amince da taimakawa sojojin Habasha a yankin Tigray

Eritrea ta amince da kasancewar ta a yankin Tigray na kasar Habasha wajen shiga cikin rikicin da sojojin gwamnati suka fafata da ‘yan awaren yankin dake neman ballewa.

Wani mayaki a yankin Tigray na kasar Habasha kan iyaka da Eritrea,ranar 22 ga watan Nuwambar 2020
Wani mayaki a yankin Tigray na kasar Habasha kan iyaka da Eritrea,ranar 22 ga watan Nuwambar 2020 EDUARDO SOTERAS AFP
Talla

Eritea ta tabbatar da hakan ne karon farko ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya jiya Juma’a, inda ta amince ta fara janye dakarunta daga yankin na Tigray dake Habasha, bayan taimakawa dakarun Abiy Ahmad.

Amincewar cikin wata wasika zuwa ga mambobin kwamitin 15 - wanda kuma ma'aikatar yada labarai ta Eritrea ta sanya a intanet - ya zo ne kwana daya bayan da shugaban agaji na Majalisar Dinkin Duniya Mark Lowcock ya ce, ba su ga wata hujja da ke nuna cewa sojojin Eritrea sun janye  daga yankin ba.

Eritiriya ta sha musanta batun a baya

Sojojin Eritiriya sun taimakawa sojojin gwamnatin tarayyar Habasha wajen yakar tsohuwar jam’iyya mai mulki ta Tigray a rikicin da ya fara a watan Nuwamba. Kodayake, Eritrea ta sha musanta cewa dakarunta suna yankin mai tsaunuka.

Firayinministan Habasha Abiy Ahmed a watan da ya gabata ya amince da kasancewar Eritriya kuma Majalisar Dinkin Duniya da Amurka sun bukaci sojojin Eritriya su fice daga Tigray.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.