Isa ga babban shafi
Zimbabwe

An binne Mugabe a Kutama

An kammala birne gawar tsohon shugaban Zimbabwe Robert Mugabe yau Asabar a kauyensa na haihuwa Kutama bayan shafe tsawon makwanni ana takaddama kan inda za a birne shi tsakanin Iyalansa da Gwamnatin kasar.

Tsohon shugaban kasar Zimbabwe marigayi Robert Mugabe.
Tsohon shugaban kasar Zimbabwe marigayi Robert Mugabe. REUTERS/Philimon Bulawayo
Talla

Bikin birne gawar Mugabe wanda ya mutu tun a farkon watan nan ya na da shekaru 95 a duniya, ya gudana ne ba tare da halartar tururuwar jama’a ba.

A ranar Juma’a Iyalan Mugabe suka yi nasarar samun izinin birne shi a kauyen da aka haife shi wato Kutama mai nisan kilomita 90 daga Harare babban birnin kasar ta Zimbabwe.

Marigayi Robert Gabriel Mugabe wanda aka Haifa a yankin Kutama, na kudancin Rhodesia (kasar Zimbabwe a yanzu) ranar 21 ga watan Fabarairun 1924 ya yi kaurin suna ne sanadiyyar kakkarfar kiyayyar da ya nuna ga turawan mulkin mallaka bayan gwagwarmayarsa ta neman ‘yanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.